Saturday, August 29, 2009

Yadda Mutuwa Ta Yi Dirar Mikiya A Gidan Marubuciya Lubabah

Mutuwa da ake yiwa lakabi da riga ce ba ta fita ga kowa. Wata babbar aya ce daga mahaliccin kowa da komai da ya ke saukar da ita ga wanda Ya so, a lokacin da Ya so, ba kuma tare da shawartar mutum ba, walau da ciwo ko ba ciwo a tafi. Aba ce mai radadi, mai firgitarwa, mai jefa zukatan bayi cikin yanayin alhini da matsananciyar dawuwa. Kana kuma ma'abociyar yanke kiyayya ko kauna. Kamar yadda ta yanke igiyar kaunar da ke tsakanin marubuci Ibrashim Sheme da matarsa marubiya Binta Salma Muhammad. Kazalika yadda ta kawo karshen soyayya tsakanin marubuci Yaron Malam da ahalinsa. Kana kuma kamar yadda ta raba marubuciya Sadiya Garba Yakasai da danta.


Kansakalin na mutuwa ya zama Sila tare da datse igiyar soyayyar marubuciya Lubabah da 'yarta Rukayya Adamu (Murfat), ba da dadewa ba, ta dawo tare da kara karbar ran wani daga cikin 'ya'yan na ta Dawud Adamu (Anis). Bata kammala warwarewa daga matsanancin alhinin rabuwa da su ba, sai mutuwar ta sake kwankwasa mata kofa. Yaya Kenan? Wannan karon ma ran wani dan nata ta kara daukewa Hamisu Adamu (Abba). Da ace marubuciyar Ilham na da ikon hana mutuwa kara kwankwasa kofar gidanta, da ko shakka babu babu abinda da baza ta iya yi domin yin katangar karfe tsakaninta da ita ba. Duk da so shu'umi ne, mutuwar sai da ta yanke wanda ke tsakanin Lubabah da mijinta Ado Dauda Bichi.


Da ba don zurfafa imani da kaddara ba, ba mamaki batan basira ya sanya Lubabah ta yi zargin wani abu. Amma sanin cewar, wanda ya daka ta bado shi ruwa ya kan ci, sai ta dau halin girma, tare da fauwala komai ga wanda ya busa musu numfashin. Ta kuma kudire a ranta cewar, Kema haka zata iya faruwa a gareki. Bayan farfadowa daga halin zulumi da alhini gami kewar da ta kasance, a halin yanzu ta bankade labulen da ya yi mata shamaki da dakatar da rubutu da tayi a baya. Ta sake sakin wani sabon littafi sabanin tsintacciyar Mage, wanda ya ce namiji uba da kishin balbal. Maje El-Hajeej Hotoro ya ziyarci Lubabah, tare da tattaunawa da ita kamar haka:


A kwanakin baya kin rasa uku daga cikin 'ya'yanki ko za ki bayyana mana yadda abin ya faru?


Hakika na rasa yarana uku kusan lokaci guda, wanda wannan wani hukunci ne na ubangiji ne da ya kan jarabci bawa a duk lokacin da Ya so. Kuma wani hukunci ne da Shi Ya fi kowa sanin dalilin hakan.


Ko lokaci guda suka rasu?


Ba lokaci guda suka rasu ba. Tsakanin daya da daya kwana 42 ne, daya kuma shekara daya da wata shida.


Silar rasuwarsu fa?


Rukayya Adamu (Murfat) ta dan yi hadari ne. Dawud Adamu (Anis) rashin lafiya ya yi na kusan tsawon kwana shida, harma ya warware Allah Ya karbi abin Sa. Shi kuma Hamisu Adamu (Abba) heater ya taba ta dafa ruwan zafi, hakan ya zama sanadiyyar Allah Ya karbi abin Sa.


Bayan wadannan daga baya ma kin kara rasa maigidanki Ado Dauda Bichi. Ko yaya kika samu kanki?


Wannan duk cikin hukunci ne na ubangiji wanda Ya shirya duk wannan daki-daki.


Yaya zaki iya bayyana yanayin da kika kasance?


Gaskiya na shiga tashin hankali, na kuma dimauta da wannan al'amari. Amma imani da kaddara ya sani yiwa kaina fada. Domin a lokacin har na yankewa kaina kauna, gani na ke yi bazan kara samun wani farin ciki ba. Amma abune da Allah ne Ya ke dorawa bawa, kuma Shi Ya san yadda zai fitar da shi. Ban kuma san wane tanadi Allah Ya Yi min a gaba ba.


Ko hakan ya shafi harkar rubutunki?


Gaskiya ya shafa. Saboda bayan faruwar hakan komai ya fice daga raina, sai kwanan nan ne ma na dan dawo harkar.


Kusan yawanci marubuta kan so rubuta labarin wani abu da ya faru akansu. Ko kin yi sha'awar mayar da wannan abu da ya faru a gareki zuwa littafi?


Gaskiya ban yi sha'awa ba.


Dalili?


Saboda ban taba daukar wani abu da ya shafi rayuwata na mayar da shi littafi ba. Duk da dai cewar ya kamata a rubuta hakan domin nunawa mutane muhimmancin hakuri, yadda Allah Ya kan jarrabi bawansa da sauransu, amma ban yi sha'awar mayar da shi littafi ba.


Ko yaya zaki bayyana rayuwarki a halin yanzu?


Na san dole ka riga ka yi aure, ka zauna da mijinka amma yau babu shi, wataran zaka zauna ka yi tunani ko wani abu haka. Amma a halin yanzu ina cikin kwanciyar hankali babu kuma wata damuwa a tare da ni.


Kin ci gaba da rubutu kenan?


Yanzu ma na ci gaba da rubutu, domin na fitar da sabon littafi.


Sunansa?


Labule.


Tasarifi

Gidajen Rawa Tsirara A Kano?



Rawar na gudana ne a yayin da suke bin kidansu dake tashi wanda ake kadawa a wajen. Kuma matan na yin rawar ne sanye da shu'man tufafi ma'abota bayyanar da surorinsu. Kamar yadda wani da yake zuwa wajen ya tabbatar min, akwai yanayin wata rawa da matan ke yi da ake kira da turanci (Ass down) wani salo ne da matan kan janyo wandonsu kasa, domin bayyanar da wani sashi na duwawunsu, kana kuma daga gaba a samu damar ganin wani sashi na mararta.

A yayin da kida yayi kida matan na girgiza sassan jikinsu, su kuma mahalarta taron zasu rika kwarara ihu. Lokaci guda kuma suna farke bandir din kudi suna faman liki ba kakkautawa. Da dama daga cikin matan matasa ne kuma baligi farare kalkal, masu kyan diri da cikar halitta. Wanda dama Malam Bahaushe da aljanun son farar mace, ballantana kuma mutumin Kano! Wata majiyar ma ta tabbatar min da cewar, wani lokacin matan har sukan fayyace nonuwansu a zahiri. Ko kuma duwawunansu kacokam ga mutane.

Wani mahalarcin wajen ya shawarci wadanda basu fara zuwa wajen ba da su rufawa kansu asiri, domin a cewarsa, kallon rawar na da matukar nishadi. Kuma idan mutum ya fara, da wahala ya daina. Kuma irin wannan rawa ta samu karbuwa sosai a wajen matasa da kuma magidantan da sukan raba dare suna nishadantuwa da kallon tsiraicin fararen matan. Kana kuma matan na gabatar da kansu ga duk mai bukata matukar sun daidaita farashi. A church road, Enugu road da kuma Ecowas duk suna gudanar da wannan rawa. Kazalika suna yi sau biyu a otal din Royal Tropicana. Kamar yadda bincike ya tabbatar. Hukumar tace fina-finai da dab'i ta jihara ita ce ke da alhakin kulawa da harkar kade-kade da wake-wake da kuma raye-raye, na kuma yi tattaki hukumar tare da ganawa da babban darakta Malam Rabo Abubakar.

A kwanakin baya wannan hukumar ta bayar sanarwa a kafafen yada labarai na tabbacin kama wasu mata na rawa tsirara a wani gidan rawa da ke unguwar Sabon Gari. Ina gaskiyar wannan batu?

Babu wani gida wararre guda daya da wanna hukuma ta taba bayar da sanarwa akansa. Gaskiya ne wannan hukuma tare da hadin gwiwar 'yan sanda da kuma kotu muna fita domin sa ido, wata fitar kuma dama muna da cikakken yakini na ana yin raye-rayen da suka sabawa shari'ah wadanda muke kira na batsa ko na badala. To a Sabon Gari irin wannan gidajen sun fi sau shurin masaki. Adadi mai yawa. Allah Ya banu iko mun yi aiki a kansu. Kuma 'yan jaridu sun dauki irin layin da suke so sun bada rahoto yadda suka fahimci lamarin.

Amma mu namu mu kama masu laifi babu cikin Sabon Gari, babu cikin gari babu wajen gari, lallai duk inda muka samu mai laifi zamu yi kokarin kamawa.

Rahotanni daga Sabon Gari sun tabbatar da akwai ire-iren wadannan gidaje da wasu 'yan kasar Chadi da Sudan ke rawa tsirara. Ko wannan rahoto ya zo muku?

Rahoto ko mutanen Nijeriya ne ko baki ne ya fi kama da hurumin wasu hukumomin. Raye-raye ko Baturen Ingila ne ya shigo cikin Kano, kasancewar an hana rawar batsa ba zamu kyale ba. Wannan rahoto shine ya ke bamu cikakken kwarin gwiwa na binciken da muka fara na wasu gidaje da har yanzu su akwai ragowar irin wannan rawa, suna fakewa da sunan na al'adarsu ne ko na gargajiyarsu ne. Kuma wannan abin da ya taso shi zai kara mana kaimi da hadin gwiwar jami'an tsaro musamman na farin kaya domin mu samu cikakken rahoto kafin mu kai garesu. Saboda na baya da muka yi, duk haka muka yi. Sai mun tara cikakkiyar hujja da bayanan da idan mun kai kara ba zamu fadi ba.

Zuwa yanzu ko kun rufe irin wannan gidajen sun kai nawa?

A kwaryar Sabon Gari gidajen raye-rayen batsa da na Disco da na Gala da na Mamin da na duk abinda za a iya tunani. Har na 'yan asharalle da sauransu akalla zasu kai gidaje 48.

A yayin da kake bayyana nasarorin wannan hukuma na rufe irin wadannan gidaje a Sabon Gari a kuma gefe guda hukumar Hisbah ta alakanta wannan aiki ga hurumin hukumar bude ido da shakawa ne wannan alhaki ya rataya a wuyansu. Ba ka ganin an kana keta huruminsu?

Hukumar Hisbah ina da tabbacin ta yi muku bayani ne a bisa abinda ta sani na doka don haka zai yi wuya tayi wani jawabi da zai yi karo. Kuma nima na yarda da Hukumar Hisbah rajista da tafiyar da al'amuran na gidan wasanni ko na shakatawa a karkashin hukumar Tourism yake. Amma mu inda muka shigo shine wanne irin abu ake yi a wajen shakatawar ko na bude idon? In anyi shi sabanin Shari'ah to muna da hurumi. Wannan ma ya sa komai kyan hajarka yayin kokarin sayar da ita, kai wani abu da ake kira badala ko wani sabo da ya keta dokokin wannan hukuma. Ba muna tuhumarka ya akayi ka samu rajistar sana'arka ba ne. Me ya sa aka same ka ka aikata ba daidai ba? Don haka muna da hurumi. Mu a fannin sa ido muke an yi daidai ko kuiwa a a, nan muke da hurumi.

Na garzaya ofishin hukumar shige da fice ta jihar inda na samu jami'in hulda da jama'a Nasiru Umar, wanda ya tabbatar min da wanzuwar wadannan mata. A zuwan farko na tarar sun kama wasu da tuni suka hankada keyarsu zuwa kasarsu. Yayin a zuwa na biyu nayi sa'ar samun wata matashiya mai suna Maryam, wacce ko ina na jikinta duk ta zane tatas da zanen furannin da ake kwalliya dasu na lalle a hannu da kafa. Na tambayi Maryam ko daga ina take ta ce daga jihar Maiduguri. Zancen da jam9i'in hulda da jama'ar ya nemi ta bashi lambar wayar mahaifi ko mahaifiyarta su kira indai sun tabbatar daga can ta ke zasu sake ta. Sai ta amsa da cewar, ta yar da wayarta. Da na tambayeta a ina suka kamo ta? Sai ta amsa da cewar church road. Me ake yi a wajen ta ce gidan rawa ne.

A binciken da na yi a wajen, na gano cewar, matan suna shigowa Nijeriya ne domin yin karuwanci. Domin akwai wacce ta bayar da tabbacin a kullum maza shida ne suke nemanta akan N500 kowane. Wanda hakan ya sa take samun jimlar N3,000 kullum. N90,000 a wata. A karo na uku ne da na koma nayi sa'ar an kamo su da dama. Inda har na shiga cikin ayarinsu a inda ake ajiye su kafin a mayar da su kasarsu. Farare ne sosai, wanda har wasu daga cikinsu na kara tasirin hasken nasu ta hanyar shafe-shafe. Daga cikinsu na tattauna da wata a takaice.

Yaya sunanki?

Zam zam.

Daga ina kike?

Chadi.

Ko kina da takardar izinin shigowa Nijeriya?

Babu.

Me ya kawo ki Nijeriya?

Yawo.

Sai dai ko kadan ban ga wani alamun damuwa tattare da su ba na kama su din da aka yi. Domin a bincikena na gano cewar da zarar an damka su ga hannun ofishin jakadancin kasar Chadi, sai su kara tsallakowa su dawo. Kuma na gano yadda wasu manyan masu fada aji na jihar ke karbarsu a hannun jami'an shige da ficen a duk sa'ad da suka kamo su. Domin ko a lokacin na samu tabbacin wani mai rawani da ya aike da katinsa na a saki wata daga ciki. Jami'in hulda da jama'ar ya koka matuka da wannan karuwanci da suke yi, domin kamar yadda ya fada akwai yiyuwar yaduwar miyagun cututtuka. A takaice ma har shaida min yayi cewar, ba irin rokon da basa yiwa matan su nemo mazan aure su kuma zasu barsu su zauna a kasar, idan barinta ne basa son yi.

Daga karshe na samu kididdigar hukumar tayi nasarar cafke adadin matan guda 16, daga watan Afirilun wannan shekarar zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Wednesday, August 26, 2009

Alkawarin Allah

Hajiya Siyama Ado Bayero 'ya ce ga mai martaba sarkin Kano, wacce ta rubuta littattafai da dama. Daga ciki shine Alkawarin Allah, wanda ya dade da fita kasuwa, kuma littafin yana dauke ne da labarin yadda samari suke amfani da hatsabiban kwayoyi domin zautar da 'yan mata, suna saduwa da su.

SHU'ARA


Shu'ara wani kayataccen littafi ne na marubi Maje El-Hajeej Hotoro, wanda ya fita kasuwa da jimawa. Yana kuma dauke da abubuwan al'aji tare da nishadantarwa. An rubuta littafin cikin salon sarrafa harshe, tare da wasa kwakwalwa. Labari ne na tausayi, soyayya, yaudara, hargitsi, da kuma butulci gami da yafiya.

Kankana

Kankana shima wani littafi ne daga cikin litattafan Marubuci Maje El-Hajeej Hotoro, wanda aka rubuta shi cikin salon jan hankali da kuma nishadi. Littafin ya samu karbuwa matukar gaske, har ta kai marubucin yayi nasarar samu cin gasa da aka gudanar a Abuja. A cikinsa akwai labarin yadda matsanancin kwadayi ke sa mata yin amfani da sirrin Kankana domi mallake duk namijin da ya kusance su. Ga kuma cin amanar yin soyayya da dan mijin da suke aure, baya kuma ga son mallake dukiyar mijin ta hanyar yaudara.

Garkuwar Nakasassu frowns at food price hike

Wife of the Kano state governor, Hajiya Halima Ibrahim Shekarau, Garkuwar Nakasassu has called on businessmen and industrialists in the state and beyond to look at the possibility of reducing the prices of essential commodities especially during the month of Ramadan.




She made the call in a meeting with representatives of some industrialists, the business community, the Ulama among other stakeholders at the Government House, Kano.



The Garkuwar Nakasassu stressed the need for all to show concern as well as make an input in ensuring sanity in the business sector particularly as it affects the pricing of essential commodities, lamenting that such price rise usually becomes so visible during the month of Ramadan; the trend that she prayed should be controlled.



She disclosed that the aim of the meeting was to brainstorm with the stakeholders with a view to looking into all the possible ways of addressing the problems of the price hike, saying that the government is always ready to contribute its quota in that direction.



In his response, representative of Dangote Group of companies, Alhaji Wafa Dantata, attributed the problem of the pricing of commodities to certain factors to include the cost of raw materials and production, saying Dangote Group has never increased a single kobo on the prices of their commodities.



On the issue of the persistence increase in the exchange rate of foreign currencies to Naira which most businessmen pretend to be among the reasons for the cost of their commodities, an elder in the WAPA market, Malam Hassan Muhammad, revealed that such increase was a problem from the Central Bank of Nigeria (CBN) and other government authorities, saying this is supposed to be addressed for the benefit of the common man.



He reiterated the determination of their companies to continue to assist the less-privileged in the society so that they will continue to have a sense of belonging as human beings.



On his part, a renowned scholar in the state, Sheikh Ibrahim Khaleel who called on all in the business and production cycles to always have the fear of God in whatever they do, also stressed the need for a price control mechanism that will dictate how such commodities will be priced as against the present trend of allowing market forces to determine the prices.



In his remark, Uztaz Tijjani Bala Kalarawi drew the attention of those concerned with the issue of pricing as well as the wholesellers and retailers to always be considerate and fear Allah in their dealings, lamenting that most of the times such price increase is being fuelled by the press as making certain reports incite others to hoard and increase the prices.



Speaking at the occasion, Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara who commended the wife of the governor for her foresight in calling for such an important meeting, tasked the Ulama not to relent in educating those concerned with the plight of the poor.



During the meeting, representatives of various trade unions in the state who spoke, including that of fruit sellers at Yan Lemo Market, Alhaji Mu’azu Yaro Gabasawa, tried to exonerate themselves from the blames for the unnecessary price increase in the prices of commodities in the state especially during the fasting period.

President Return


President Umaru Musa Yar'Adua returned from his 10-day medical check-up in Saudi Arabia yesterday, where he also performed the lesser Hajj (Umra).




Barely a few hours after arriving the Aso Rock Villa, the president responded to media reports, which alleged that his ongoing civil service reforms were anti-north and a promotion of a southern agenda.



The president equally dismissed claims of northernisation of the nation's banking sector, as alleged by some southerners, through the government's action in which some bank executives were indicted for sharp practices.



A national daily had reported yesterday that the reforms being implemented by the new Head of Service, Mr Steven Oronsaye, were aimed at frustrating the upward movement of northerners in the federal bureaucracy in favour of southerners.



In the case of the Central Bank of Nigeria, the presidency defended the reform initiated by the governor of the apex bank, Malam Sanusi Lamido Sanusi, saying it was intended to restore sanity to the industry and add value to investor's interest.



Speaking to State House correspondents through his spokesman, Mr Olusegun Adeniyi, Yar'Adua decried a continuous linkage of every public policy to ethnicity, saying that every well-meaning Nigerian must be wary of the resurfacing of ethnic politics in the nation's polity.



He said the primary purpose of introducing the tenure system was to institute due process in the appointment of directors and permanent secretaries, arrest the succession crisis in the service, create vacancies, reinvigorate the system, and boost the morale of qualified and deserving officers.



According to Adeniyi, Yar'Adua was not happy with the new trend of ethnicisation of politics and politicisation of ethnicity in Nigeria, and wondered why the introduction of tenure for permanent secretaries and directors in the Federal Civil Service should be a thing of apprehension when the exercise "is already boosting morale within the system."



The presidency was particularly irked by those it believed were out to misrepresent the facts contained in the approval granted by the president.



Adeniyi said: "What is particularly unfortunate is the recourse to ethnicity whenever some interests are affected by crucial decisions taken in promotion of national well-being.



"While no one has faulted the exercise, there is now a whispering campaign that it is targeted against the North simply because the Head of the Civil Service of the Federation, Mr. Steve Oronsaye, is from Edo State; the same way those affected by the banking reform would argue it is targeted against the South because the CBN Governor, Mr Sanusi Lamido Sanusi, hails from Kano!"



He added, "While the Nigerian civil service has undergone several reforms and will continue to undergo reforms in conformity with the ever-changing times and circumstances, the latest exercise, which has been approved by President Umaru Musa Yar'Adua, is the tenure for permanent secretaries and directors in the Federal Civil Service."

Tuesday, August 25, 2009

Laifin Me Mazauna Darul Islam Suka Yi?


Ina fatattakar 'yan Darul-Islam da gwamnati tayi? Laifinsu kawai shine domin sun zabi kauracewa daga cikin mutane da suke ganin tarbiyya ta lalace sun zabi komawa wajen gari su gudanar da addininsu gwargwadon fahimtarsu? Fahimta fuska ce. Kuma kundin tsarin mulkin kasa yabawa kowa 'yancin zabin addini. Ko kadangare mutum ya ce zai bautawa yana da wannan hakkin. Duk binciken da aka gudanar ya nuna mutanen nan basu da alaka da kungiyar boko haram. Suna ma da makaranta a yankin dake koyar da karatun boko. An kuam saka koyarwa a sashin Hausa na BBC duniya taji, yayin da wakilinsu ya gudanar da bincike na musamman a garin.



Mutanen nan da kansu suka nemi hukuma ta kai rangadi tare da gudanar da duk binciken da ya dace. Daga gida zuwa gida aka rika bincike ba a same su da makamai ba. An tintubi makotansu sun bayar da shaidar mutane ne masu son zama lafiya. Babu kuma wani yamutsi da ya taba hada su da kowa, tsawon shekaru 17 da suka yi a wajen. Suna tsaka da sallar asubashi jami'an tsaro suka tattare su tare da kai su wata makaranta aka rika bincikensu na tsawon wani lokaci. A cewar wani shugabansu yayin da ake tattaunawa dashi ta wayar salula washegari, ya bayyana cewar, wajen da aka ajiye su, babu abinci, babu wajen kewayawa, babu cikakkiyar kulawa, ga yara kwance a kasa ba lafiya. Hakkin bil Adama kenan?


Ina tanadin dokar kasa sashi na 41 da ya bawa kowane dan kasa 'yancin walwala da yawatawa a kowane yankin na kasar? Babu wata doka daga cikin tsarin kundin mulkin 1999 da ya bayar da izinin kama mutum haka kawai don ya zabi zama a wani yankin Nijeriya matukar dan kasa ne. A sashi na 46 na kundin tsarin mulkin kasar nan ya hana a tashi dan kasa daga wani yanki da ya zabi zama, sai dai a kai shi kotu. Kuma ko da kotun ta nemi ya tashi daga wajen, sai an biya shi diyya. Mutanen nan manoma ne, sunyi shuka, basu girbe ba, an tarkata su, an mayar da su inda suka fito. Ba tare da umarnin kotu ba, ba tare da an biya su diyya ba. Ina hakkin bil Adama?


Hala gwamnati bata tunanin wannan wani sabon salon barna suka bude? Domin idan sun mayar dasu inda suke, me suka tanadar musu? Me zasu rika yi a can? Ba sa tunanin sauya musu tunani daga masoya zaman lafiya, zuwa masoya neman ramuwar gayya wacce tafi ta gayya zafi ko ba dade ka ba jima? Kuma ko ta wacce hanya? Ba sa tunanin nan gaba irin wadannan mutanen da aka gallazawa bama kungiyar boko haram ba, ko kungiyar ci da sha haram, aka gayyace su zasu iya mika wuya? Basa tunanin nan gaba kowane gwamna zai iya kafa hujja da wannan dalili a gaba ya kori duk bakin johohin mazauna jiharsa, musamman ma idan suka samu bambanci ra'ayin siyasa? Basa tunanin ire-iren dangogin wadannan take haddi ne, ya haifar da ambaliyar kunar bakin-wake da 'yan bindiga dadi da yau suka zamewa duniya alakakai?